Перейти к содержимому

05 "Shawwal "Tafsirin Al-qur'ani (Suratul Nisa'i) Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam 2003" #sunnah

Al arham 1

0:00 / 0:00

05 "Shawwal "Tafsirin Al-qur'ani (Suratul Nisa'i) Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam 2003" #sunnah

14 832 просмотра · 5 месяцев назад
Al arham 1
2,9 тыс. подписчиков
14 832 просмотра · 5 месяцев назад
; Ya ku mutane! Ku bi Ubangijinku da takawa Wanda Ya halitta ku daga rai guda, kuma Ya halitta, daga gare shi, ma´auransa, kuma Ya watsa daga gare su maza masu yawa da mata. Kuma ku bi Allah da takawa Wanda kuke rokon juna da (sunan), shi, da kuma zumunta. Lalle ne Allah Ya kasance, a kanku, Mai tsaro ne. 2; Kuma ku bai wa marayu dukiyoyinsu, kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau. Kuma kada ku ci dukiyoyinsu zuwa ga dukiyoyinku. Lalle shi, ya kasance zunubi ne mai girma. 3; Kuma idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba a cikin marayu, to, (akwai yadda za a yi) ku auri abin da ya yi muku dadi daga mata; biyu-biyu, da uku-uku, da hudu-hudu. Sa´an nan idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa abin da hannayenku na dama suka mallaka. Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku wuce haddi ba. 4; Kuma ku bai wa mata sadakokinsu da saukin bayarwa. Sa´an nan idan suka yafe muku wani abu daga gare shi, da dadin rai, to, ku ci shi da jin dadi da saukin hadiya. 5; Kada ku bai wa wawaye dukiyarku, wadda Allah Ya sanya ta a gare ku, kuna masu tsayuwa (ga gyaranta). Kuma ku ciyar da su a cikinta, kuma ku tufatar da su, kuma ku gaya musu magana sananniya ta alheri. 6; Kuma ku jarraba marayu, har a lokacin da suka isa aure. To, idan kun lura da shiriya daga gare su, to, ku mika musu dukiyoyinsu. Kada ku ci ta da barna, kuma da gaggawa kafin su girma. Kuma wanda yake wadatacce, to, ya kama kansa, kuma wanda yake fakiri, to, ya ci, gwargwadon yadda ya kamata. To, idan kun mika musu dukiyoyinsu, sai ku shaidar a kansu. Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai bincike. 7; Maza suna da rabo daga abin da iyaye biyu da mafi kusantar dangi suka bari, kuma mata suna da rabo daga abin da iyaye biyu da mafi kusantar dangi suka bari, daga abin da ya karanta daga gare shi ko kuwa ya yi yawa, rabo yankakke. 8; Kuma idan ma´abuta zumunta da marayu da matalauta suka halarci rabon, to, ku azurta su daga gare shi, kuma ku fada musu magana sananniya ta alheri. 9; Kuma wadanda suke da sun bar zuriyya masu rauni a bayansu, za su ji tsoro a kansu, su yi sauna, sa´an nan su bi Allah da takawa, kuma su fadi magana madaidaiciya. 10; Lalle ne, wadanda suke cin dukiyar marayu da zalunci, to, wuta kawai suke ci a cikin cikkunansu, kuma za su shiga cikin wata wuta mai tsanani. 11; Allah Yana yi muku wasiyya a cikin ´ya´yanku; namiji yana da rabon mata biyu. Idan sun kasance mata ne fiye da biyu kuwa, to, suna da biyu daga kashi uku din abin da ya bari, kuma idan ta zama guda ce (kawai) to, tana da rabi. Kuma iyayensa biyu kowane daya daga cikinsu yana da daya daga kashi shida din abin da ya bari idan wani rhshe ya kasance gare shi, to, idan rhshe bai kasance gare shi ba, kuma iyayensa ne (kawai) suka gaje shi, to, uwa tana da sulusi (daya daga cikin kashi uku). Sa´an nan idan ´yan´uwa sun kasance gare shi, to, uwarsa tana da sudusi (daya daga cikin kashi shida) daga bayan wasiyya wadda ya yi ko kuwa bashi. Ubanninku da ´ya´yan ku, ba ku sani ba, wannensu ne mafi kusantar amfani, a gare ku. Yankawa daga Allah. Lalle ne, Allah Ya kasance Masani Mai hikima. 12; Kuma kuna da rabin abin da matanku na aure suka bari idan rhshe bai kasance gare su ba. Sa´an nan idan rhshe ya kasance gare su, to, kuna da rubu´i (daya daga cikin kashi hudu) daga abin da suka barin, daga bayan wasiyya wadda suka yi ko kuma bashi. (Su) kuma suna da rubu´i daga abin da kuka bari idan rhshe bai kasance ba gare ku, idan kuwa rhshe ya kasance gare ku, to, suna da sumuni (daya daga cikin kashi takwas) daga abin da kuka bari, daga bayan wasiyya wadda kuka yi ko kuwa bashi. Idan wani namiji ya kasance ana gadon sa bisa kalala, ko kuwa wata mace alhali kuwa yana da dan´uwa ko ´yar´uwa to, kowane daya daga cikinsu yana da sudusi (daya daga cikin kashi shida), sai idan sun kasance mafi yawa daga wannan, to, su abokan tarayya ne a cikinsulusi (daya bisa uku), daga bayan wasiyya wadda aka yi ko kuma bashi. Ba da yana mai cutarwa ba, ga wasiyya, daga Allah. Kuma Allah Masani ne Mai hakuri. 13; Wadancan iyakokin Allah ne. Wanda ya yi da´a ga Allah da ManzonSa, (Allah) zai shigar da shi gidajen Aljanna (wadanda) doramu suna gudana daga karkashinsu, suna madawwama a cikinsu, kuma wannan shi ne rabo babba. 14; Kuma wanda ya saba wa Allah da ManzonSa, kuma ya. #sunnah #arewa #lifeisbutadream #quranchapter #kannywood #bakoritv #sairamovie #africatv3