Перейти к содержимому

An bukaci Hisbah ta sa baki kan aure-auren Adam Zango

Madubi TV

0:00 / 0:00

An bukaci Hisbah ta sa baki kan aure-auren Adam Zango

4 842 просмотра · 1 месяц назад
Madubi TV
131 тыс. подписчиков
4 842 просмотра · 1 месяц назад
Wani fitaccen mai tasiri a kafafen sada zumunta, Aliyu Dahiru Aliyu, ya jawo ce-ce-ku-ce bayan ya yi tsokaci kan rahotannin da ke yawo cewa jarumin Kannywood Adam A. Zango ya sake matarsa. A cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Aliyu ya yi kakkausar suka kan yawan auren da ake dangantawa da Adam Zango, inda ya yi kira ga Hukumar Hisbah da ta dauki mataki kan lamarin. Ya bayyana cewa idan har ana yawan aure da saki, hakan na iya rage darajar aure a idon jama'a. Kalaman nasa sun bazu sosai a kafafen sada zumunta, inda wasu suka goyi bayansa, yayin da wasu kuma suka ce bai dace a yi irin wannan magana ba, suna ganin lamarin na Adam Zango ne da iyalansa. Ku fa, mene ne ra'ayinku? Shin ya dace Hisbah ta sa baki a irin wannan lamari, ko kuwa al'amari ne na kashin kai? Madubi TV – Ku danna Subscribe sannan ku kunna kararrawa domin samun sabbin labarai cikin gaggawa.